A yau ne aka bude bikin baje kolin wayar tarho na kasa da kasa karo na 8 na kudancin kasar Sin (Humen), wanda aka kwashe tsawon kwanaki 3 ana yi a cibiyar baje kolin kayayyakin tarihi ta Humen da ke birnin Dongguan. Kusan kamfanoni 200 daga ko'ina cikin kasar ne suka halarci baje kolin tare da sabbin kayayyaki da fasahohinsu.